📖 Zabura 81
-
1
Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
-
2
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
-
3
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
-
4
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
-
5
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
-
6
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an ’yantar da hannuwansu daga kwando.
-
7
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. Sela
-
8
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
-
9
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
-
10
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
-
11
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
-
12
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
-
13
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
-
14
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
-
15
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
-
16
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”