📖 Zabura 3
-
1
Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
-
2
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” Sela
-
3
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
-
4
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. Sela
-
5
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
-
6
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
-
7
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
-
8
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. Sela