📖 Zabura 109
-
1
Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
-
2
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
-
3
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
-
4
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
-
5
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
-
6
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
-
7
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
-
8
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
-
9
Bari ’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
-
10
Bari ’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
-
11
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
-
12
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
-
13
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
-
14
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
-
15
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
-
16
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
-
17
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
-
18
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
-
19
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
-
20
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
-
21
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
-
22
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
-
23
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
-
24
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
-
25
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
-
26
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
-
27
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
-
28
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
-
29
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
-
30
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
-
31
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.