📖 Zabura 102
-
1
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
-
2
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
-
3
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
-
4
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
-
5
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
-
6
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
-
7
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
-
8
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
-
9
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
-
10
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
-
11
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
-
12
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
-
13
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
-
14
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
-
15
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
-
16
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
-
17
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
-
18
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
-
19
“ Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
-
20
don yă ji nishe-nishen ’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
-
21
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
-
22
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
-
23
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
-
24
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
-
25
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
-
26
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
-
27
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
-
28
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”