📖 Ayuba 6
-
1
¶ Sa’an nan Ayuba ya amsa,
-
2
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
-
3
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
-
4
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
-
5
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
-
6
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
-
7
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
-
8
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
-
9
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
-
10
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
-
11
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
-
12
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
-
13
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
-
14
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
-
15
Amma ’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
-
16
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
-
17
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
-
18
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
-
19
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya ’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
-
20
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
-
21
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
-
22
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
-
23
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
-
24
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
-
25
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
-
26
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
-
27
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
-
28
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
-
29
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
-
30
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?