📖 Ayuba 40
-
1
¶ Ubangiji ya ce wa Ayuba,
-
2
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
-
3
¶ Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
-
4
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
-
5
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
-
6
¶ Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
-
7
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
-
8
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
-
9
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
-
10
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
-
11
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
-
12
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
-
13
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
-
14
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
-
15
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
-
16
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
-
17
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
-
18
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
-
19
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
-
20
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
-
21
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
-
22
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
-
23
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
-
24
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?