📖 Ayuba 25
-
1
¶ Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
-
2
“Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
-
3
Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
-
4
Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
-
5
In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
-
6
mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”